Najeriya ta tabbatar da bullar Coronavirus a Lagos

Cutar Corononavirus

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Najeriya ta shiga jerin kasashe 48 da cutar coronavirus ta bulla

Hukumomi a Najeriya sun tabbatar da bullar cutar coronavirus da ake kira Covid-19 a jihar Lagos.

Ma'aikatar lafiya ce ta tabbatar da bullar cutar a sanarwar da ta wallafa a Twitter, inda ta ce a karon farko an samu bullar cutar a Najeriya tun barkewarta a China a watan Janairun 2020.

Kauce wa Twitter, 1
Ya kamata a bar bayanan Twitter?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da Twitter suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Twitter da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1

Haka ma cibiyar da ke yaki da cututuka masu yaduwa a Najeriya ta wallafa a Twitter inda ta ce ministan lafiya ya tabbatar da bullar cutar a jihar Lagos.

Kauce wa Twitter, 2
Ya kamata a bar bayanan Twitter?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da Twitter suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Twitter da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 2

A sanarwar da ya fitar, ministan lafiya na Najeriya Dr Osagie Ehanire ya ce wani dan Italiya ne da ke aiki a kasar ya shigo da cutar bayan ya dawo daga Milan zuwa Lagos.

"Sakamakon gwaji da aka gudanar a asibitin koyarwa na jami'ar Lagos ya tabbatar da yana dauke da cutar."

"Ana duba lafiyarsa a asibitin kula da cutuka masu yaduwa a Yaba, kuma marar lafiyar bai nuna alamomi masu muni ba," in ji shi.

Ya kuma ce gwamnati ta kara tsaurara matakai domin tabbatar da dakile yaduwar cutar.

Tun a ranar Laraba ne ake ta yada jita-jitar labarin bullar cutar a Lagos a shafukan intanet bayan kwantar da wani dan China a asibitin Reddington da ke Ikeja.

Daga baya asibitin ya karyata labarin amma bai musanta zuwan dan China ba a asibitin domin diba lafiyarsa da ake fargabar yana dauke da cutar mai yin kisa a China.

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce cutar coronavirus ta kai wani matsayi na zama annoba a duniya saboda yadda take yaduwa.

Najeriya yanzu ta shiga jerin kasashen duniya da aka samu bullar cutar ta da ake kira COVID-19, kasa ta uku da aka samu bullarta a Afirka bayan Masar da Aljeriya.